Home General Bello Turji ya bayyana aniyar mika wuya – Manjo janar Christopher Musa

Bello Turji ya bayyana aniyar mika wuya – Manjo janar Christopher Musa

Babban Hafsan Sojojin Najeriya, Janar Christopher Musa a jiya Juma’a ya bayyana cewa fitaccen shugaban ‘yan ta’adda Bello Turji ya bayyana aniyar mika wuya. Ya bayyana hakan ne a lokacin da aka gayyace shi a cikinn wani shiri na gidan talabijen mai zaman kan sa a kasar.

Manjo Janar Christopher Musa, ya kara da cewa hare-haren da sojoji suka yi a baya-bayan nan, wanda ya kawar da wasu kwamandojin Turji da wasu mukarrabansa, ya karya logon shugaban ‘yan ta’addan.

Hakan ne ya tilasta masa sakin da dama daga cikin mutanen da ya yi  garkuwa da su, lamarin da ke nuni da shirinsa na ajiye makamai.

Yan ta’adda suna cikin al’umma; mutane sun san su. Don haka, wani lokacin idan sun gan su, kafin ka sami bayanin, kamar sa’o’i biyu ne – mutumin ya motsa. Don haka idan bayanin ya same ka, kafin ka matsa ya bar yankin.” Inji Janar Musa.

Ya kara da cewa, “Amma zan iya gaya muku, mun fitar da na biyu a matsayinsa, mun fitar da mafi yawan hakimansa, hasali ma ya tilastawa yanzu ya saki mafi yawan mutanen da ke karkashinsa.

Ina gaya muku kwanan nan ya fara cewa ba ya son komai, a shirye yake ya mika wuya.” Duk da cewa Turji ya bayyana aniyar mika wuya, Janar Musa ya jaddada muhimmancin daure masu aikata ta’addanci, musamman wadanda ke da alhakin mutuwar ‘yan kasa da ba su ji ba ba su gani ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp