Home General NLC ta dakatar da yin zanga-zanga Kan tsadar Data da kudin kira

NLC ta dakatar da yin zanga-zanga Kan tsadar Data da kudin kira

Kungiyar kwadago ta janye zanga Zangar da ta shirya gudanar wa a Talatar nan sakamakon Karin kudin kiran waya da na Data.

Wannan ya biyo bayan wata ganawa da ta yi da wakilan gwamnati a ofishin sakataren gwamnatin tarayya a daren Litinin, kungiyar kwadagon ta ce ta yanke shawarar dakatar da zanga-zangar har sai an dawo teburin tattaunawa.

Da yake zantawa da manema labarai bayan taron, shugaban kungiyar na kasa Joe Ajaero, ya ce gwamnati ta amince da kafa wani babban kwamiti da zai duba daukacin tsarin kudin Kiran waya.

A cewarsa, kwamitin zai kunshi wakilai biyar daga bangarorin biyu kuma ana sa ran zai mika rahoton bincikensa cikin makonni biyu.

Ya kara da cewa kungiyar za ta dauki matakan zanga-zanga da yajin aiki nan gaba, mutukar ba’a Sami wata matsaya ba kan rahoton Kwamitin .

Idan za,a iya tunawa dai a makonnin da Suka gabata ne hukumar Sadarwa ta kasa ta amincewa kamfanonin sadarwa masu zaman kanau da su kara kashi Hamsin na kudin Kiran waya da na amfani da data, wacce ta Kai ga kungiyar kwadago barazanar fita zanga zanga a ranar hudu ga watan Fabarairu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp