Home General Kotun ta yankewa mutum biyar hukuncin kisa a Kano

Kotun ta yankewa mutum biyar hukuncin kisa a Kano

Wata babbar kotu da ke Kano a Najeriya ta yanke wa wasu mutum biyar hukuncin kisa ta hanyar ratay bayan kama su da laifin kisan wata tsohuwa bisa zargin maita.

Kotun ta ce ta samu mutanen da laifin yin silar mutuwar tsohuwar mai shekara 67 a duniya a ranar 15 ga watan Nuwamban 2023, ba tare da ƙwaƙƙwarar hujja ba.

A lokacin yanke hukuncin, mai shari’a Usman Na’abba ya bayyana cewa kotun ta samu hujjoji ƙarara da suka tabbatar da laifin waɗanda ake tuhuma.

Lamarin dai ya faru ne a ƙauyen Daɗin Kowa da ke ƙaramar hukumar Wudil ta jihar Kano.

Maita da tsafi abubuwa ne da ke yawan janyo cece-ku-ce a ƙasashen Afirka, inda iyalai kan ɗauki mataki kan mutanen da suke zarga da sanadin kashe musamman yara ta hanyar maita.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp