Home General Kotun ta yankewa mutum biyar hukuncin kisa a Kano

Kotun ta yankewa mutum biyar hukuncin kisa a Kano

Wata babbar kotu da ke Kano a Najeriya ta yanke wa wasu mutum biyar hukuncin kisa ta hanyar ratay bayan kama su da laifin kisan wata tsohuwa bisa zargin maita.

Kotun ta ce ta samu mutanen da laifin yin silar mutuwar tsohuwar mai shekara 67 a duniya a ranar 15 ga watan Nuwamban 2023, ba tare da ƙwaƙƙwarar hujja ba.

A lokacin yanke hukuncin, mai shari’a Usman Na’abba ya bayyana cewa kotun ta samu hujjoji ƙarara da suka tabbatar da laifin waɗanda ake tuhuma.

Lamarin dai ya faru ne a ƙauyen Daɗin Kowa da ke ƙaramar hukumar Wudil ta jihar Kano.

Maita da tsafi abubuwa ne da ke yawan janyo cece-ku-ce a ƙasashen Afirka, inda iyalai kan ɗauki mataki kan mutanen da suke zarga da sanadin kashe musamman yara ta hanyar maita.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp