Home General Gwamnatin Najeriya ta musanta zarge-zargen rashawa da jami’in Binance ya yi wa...

Gwamnatin Najeriya ta musanta zarge-zargen rashawa da jami’in Binance ya yi wa ƙasar

Gwamnatin tarayya ta yi watsi da iƙirarin da jami’in kamfanin Binance, Tigran Gambaryan, wanda ya shafe wata takwas yana tsare a ƙasar, kan zarge-zargen rashawa.

A kwanakin baya ne aka gurfanar da Gambaryan- ɗan Amurka – a kotun Najeriya bisa zargin laifukan kuɗi.

To sai dai hukumomin Najeriya sun sake shi ne bayan shiga tsakani da gwamnatin Amurka ta yi.

Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X, Gambaryan ya yi ikirarin cewa kama shi da gwamnatin Najeriya ta yi ba bisa ƙa’ida ba ya sa tsohon shugaban ƙasar Amurka, Joe Biden ya kauce wa ganawar da ya shirya yi da Shugaban Najeriya, Bola Tinubu a yayin taron Majalisar Dinkin Duniya na 2024 (UNGA).

Ya kuma zargi mai baiwa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro, Mallam Nuhu Ribadu kan lamarin, sannan ya ce gwamnatin Amurka ta rage yawan wakilan Najeriya da suka halarci taron na MDD.

Jami’in na Binance ya kuma zargi wasu ƴan majalisar ƙasar uku da neman cin hancin dala miliyan 150 daga wajensa.

To sai dai a martanin da gwamnatin ƙasar ta mayar masa, ta ce zarge-zargen nasa ba su da tushe balle makama.

Cikin wata sanarwa da ministan yaɗa labaran ƙasar, Mohammed Idris ya fitar, ya bayyana iƙirarin Gambaryan a matsayin tsantsar ƙarya da gangan.

“Gwamnatin Najeriya ta damu matuƙa da zarge-zargen marasa tushe, da kuma kalaman ɓatanci da Tigran Gambaryan, da aka yi wa shari’a a Najeriya kwannan kan laifukan kuɗi,” a cewar sanarwar.

Ta kuma ƙara da cewa ”gwamnati ta ki amincewa da tayin da Binance ta yi na biyan dala miliyan biyar don sakin Mista Gambaryan, don yin sulhu da gwamnatin Amurka.”

A farkon shekarar da ta gabata ne dai gwamnatin Najeriya ta tsare Mista Gambaryan tare da abokin aikinsa, Nadeem Anjarwalla ɗan Kenya asalin Birtaniya mai shekara 37 bisa zargin laifukan ɓarnatar da kuɗi da hukumar EFCC ke bincike.

To amma a watan Maris ɗin shekarar Anjarwalla ya gudu daga wurin da ake tsare da su, ya kuma fice daga Najeriya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp