Home General NNPCL ya musanta zargin rashin aukin man fetur ɗin da yake sayarwa

NNPCL ya musanta zargin rashin aukin man fetur ɗin da yake sayarwa

Babban kamfanin mai na Najeriya NNPCL ya yi watsi da iƙirarin da wani mutum ya yi cewa man da kamfanin ke sayarwa bai kai na Dangote auki ba.

Cikin wani bidiyo da ya karaɗa shafukan sada zumunta an ga wani mutum da ya ce ya sayi man fetru daga kamfanin NNPCL a kan farashin naira 945, sannan ya sayi wani man a wani gidan mai da ke sauke man Dangote, a kan naira 925.

A cikin bidiyon mutumin ya yi iƙirarin cewa man Dangote ya zarta na kamfanin NNPLC daɗewa ana amfani da shi, inda har ya yi iƙirarin gwada mayukan biyu a injuna biyu, daga ƙarshe ya ce na NNPCL ya riga na Dangote ƙarewa da minituna fiye da 10.

To sai dai cikin wata sanarwar martani da NNPCL ɗin ya fitar ya ce gwajin da mutumin ya yi bai yi shi da ƙwarewa ba, sannan babu wata hujja ta kamawa a cikinsa.

Sanarwar ta kuma ƙara da cewa mafi yawan man da wannan gidan mai na NNPCL – da mutumin ya yi iƙirarin sayo man – daga kamfanin Dangote yake sayensa.

“NNPCL na jaddada ƙudirinsa na cewa man da yake sayarwa ana haɗa shi da ɗaya daga cikin manyan sidanarai masu inganci da ke taimakawa wajen tabbatar aukinsa da kuma rashin illa ga muhalli”, in ji sanarwar.

Daga ƙarshe ya gargaɗi masu irin wannan ɗabi’a cewa ba zai jure irin waɗannan ƙarairayi da ake shiryawa domin ɓata masa suna da kuma cutar da ƴan Najeriya ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp