Home General Najeriya za ta ci gaba da rike ma’aikatan lafiya dubu 28 duk...

Najeriya za ta ci gaba da rike ma’aikatan lafiya dubu 28 duk da dakatar da USAID

Gwamnatin Najeriya ta sanar da shirin ci gaba da rike ma’aikatan lafiya 28,000 da Hukumar Raya Kasashe ta Amurka USAID ke daukar nauyinsu a baya, wanda shugaban Amurka Donald Trump ya dakatar da ayyukanta.

Ministan lafiya da walwalar jama’a na Najeriya, Muhammad Pate, ya bayyana hakan, yayin hira da wata kafar talabijin ta ƙasar, inda ya bayyana cewa gwamnati na ƙoƙarin shigar da ma’aikatan cikin tsarin kiwon lafiyar ƙasar tare da rage dogaro da tallafi da ƙasashen ƙetare ke bayarwa.

Mista Pate ya bayyana gagarumar gudunmawar da gwamnatin Amurka ke bayarwa a fannin kiwon lafiyar Najeriya, musamman a bangaren cutar kanjamau, tarin fuka, da zazzabin cizon sauro, sai dai ya jaddada cewa Najeriya ta kuduri aniyar daukar nauyin sashen kula da lafiyarta da kuma rage dogaro da tallafin da take samu daga waje.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp