Home General Akpabio da Natasha: Ku yi hankali kada kimar majalisa ta zube- Saraki

Akpabio da Natasha: Ku yi hankali kada kimar majalisa ta zube- Saraki

Tsohon shugaban majalisar dattawa, Sanata Bukola Saraki ya yi kira ga dukkan ɓangarorin shugaban majalisar dattawa, Sanata Godswill Akpabio da Sanata Natasha Akpoti da su iya bakinsu domin kare martabar majalisar.

A baya-bayan nan dai shugaban Majalisar Dattawan Sanata Godswill Akpabio ya riƙa samun saɓani da Sanata Natasha, lamarin da ya sa har Natasha ta shigar da shi ƙara a gaban kotu, kan zargin ɓata mata suna.

To sai dai tsohon Shugaban Majalisar Sanata Saraki ya ja kunne duka ɓangarorin don kauce wa zubar wa majalisar kima.

Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa Facebook, Saraki ya ce abin da ya farun bai kamata ba, “wannan ya sa nake ganin ɓangarorin biyu da magoya bayansu na cikin majalisa da wajenta kowa ya iya bakinsa, kowa ya san tasirin da abin da yake aikatawa ko ya faɗa zai iya yi ga majalisar domin kare daraja da ƙimar da majalisa take da ita.”

Ya ce ya zama dole a bi dokar kundin tsarin mulki da dokokin majalisa wajen kawo ƙarshen wannan taƙaddama da ke tsakanin mutanen biyu.

“Sannan a yi komai a buɗe, ba tare da ba wa wani ɓangare fifiko ba. Abin da ya kamata a saka a gaba shi ne fito da gaskiya da kuma kare mutuncin majalisa wadda ita ce take da alhakin yin doka a ƙasa, saboda haka tana buƙatar a yi ƙoƙarin ba ta kariya da fito da mutuncinta.”

Ya ce a lokacin da yake shugaban majalisar, wani sanata ya zarge shi da fasaƙwaurin mota, “wanda hakan ya sa aka kafa kwamiti kuma a gaban ƴan jarida na kare kaina a gaban kwamitin.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp