Home General Hare-haren Sojin Somalia sun hallaka mayaƙan al Shabaab fiye da 40

Hare-haren Sojin Somalia sun hallaka mayaƙan al Shabaab fiye da 40

Wasu bayana na bayyana cewa a kalla Mayaƙan al Shabab fiye da 40 ne suka mutu a wani gumurzu tsakaninsu da dakarun Sojin Somalia a ƙarshen mako, dakarun gwamnatin dai na ci gaba da samun galabar mafi girma a baya-bayan nan.

Sanarwar da rundunar Sojin Somalia ta wallafa a shafinta na X aka kuma sanar a gidan talabijin mallakin gwamnati a daren Lahadi, ta ce dakarunta sun hallaka mayaƙan fiye da 40 a yankin Hirshabelle.

Sanarwar ta ci gaba da cewa, dakarun Sojin sun ƙaddamar da hare-haren da taimakon dakarun ƙasashe da ke taimaka musu a yaƙi da al Shabaab ta yadda suka yi musu ƙawanya a maɓoyarsu da ke Biya Cadde a yankin na Hirshabelle.

Rundunar Sojin ta Somalia ta ce har zuwa yanzu dakarun na ci gaba da luguden wuta a maɓoyar mayaƙan na al Shabaab.

A baya-bayan nan Sojojin Somalia na samun nasara kan mayaƙan al Shabaab inda ko a watan jiya ta hallaka da dama daga cikinsu kwanaki bayan Amurka ta musu luguden wuta da jiragen yaƙi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp