Home General Dalilin da ya sa muka hana Fubara shiga Majalisa

Dalilin da ya sa muka hana Fubara shiga Majalisa

Jami’an tsaron da ke gadin harabar majalisar dokokin jihar Rivers sun ƙulle ƙofar majalisar tare da hana gwamnan jihar Siminalayi Fubara shiga zauren majalisar.

Cikin wani bidiyo da sakataren yaɗa labaran gwamnan ya wallafa shafinsa na Facebook ya ce Fubara ya je majalisar ne domin gabatar da kasafin kuɗin jihar na 2025.

Rahotonni daga birnin Fatakwal sun ce tarin jami’an tsaron da aka jibge a harabar sun rufe ƙofar shiga majalisar a lokacin da gwamnan ya hallara tare da tawagarsa domin gabatar da kasafin.

Bayanai sun ambato jami’an tsaron na cewa sun yi hakan ne saboda ba a sanar da su labarin zuwan gwamnan a hukumance ba.

To sai dai Gwamna Fubara ya ce tuni ya aike wa kakakin majalisar, Martins Amaewhule wasikar sanar da shi zuwansa, kuma ya yi ƙoƙarin kiransa a waya tun ranar Talata.

A makonnin da suka gabata ne dai Kotun Ƙolin ƙasar ta yanke hukunci hana CBN bai wa jihar kason kuɗaɗenta daga tarayya saboda rashin gabatar da kasafin kuɗi a gaban halastacciyar majalisar dokokin jihar.

Haka kuma kotun ta yanke hukuncin maido da ƴanmajalisar jihar 27 da suka sauya sheƙa zuwa APC, tare da soke zaɓen ƙananan hukumomin jihar.

To sai dai a ranar 28 ga watan Fabrairu, Fubara ya sanar da yin aiki da hukuncin kotun tare da umartar hukumar zaɓen jihar ta shirya sabon zaɓen ƙananan hukumomin.

Tuni dai hukumar ta saka ranar 9 ga watan Agustan 2025 domin gudanar da sabon zaɓe.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp