Home General PSC ta amince da Nadin CP Ibrahim Adamu Bakori matsayin kwamishinan ‘yan...

PSC ta amince da Nadin CP Ibrahim Adamu Bakori matsayin kwamishinan ‘yan sandan Jihar Kano

Hukumar kula da aikin Ƴansanda ta Najeriya (PSC), ta amince da naɗa CP Ibrahim Adamu Bakori, a matsayin sabon kwamishinan ƴansandan jihar Kano.

Shugaban hukumar, DIG Hashimu Argungu mai ritaya ne ya tabbatar da naɗin inda ya nemi sabon kwamishinan da ya tabbatar da an samu zaman lafiya mai ɗorewa a jihar, ta hanyar tunkarar ƙalubalen da ke gabansa wajen tabbatar da an daƙile ƙaruwar aikata laifuka a jihar mai yawan jama’a.

CP Bakori dai zai maye gurbin CP Salman Garba Dogo ne biyo bayan samun ƙarin girma zuwa mataimakin babban sifeto na ƙasa (AIG), kamar yadda sashen Hausa na BBC ya rawaito.

Kafiin naɗin nasa, CP Bakori ya kasance kwamishinan ƴansanda mai kula da sashen binciken kisan kai (Homicide) a shelkwatar ƴansandan ƙasar da ke Abuja.

Jihar Kano dai na fama da matsalolin dabanci da ƙwacen waya da sace-sace, baya ga na baya-bayan nan wato rikicin masarautar Kano da ya janyo al’umma suka sauya tunaninsu kan rundunar ƴansandan jihar.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp