Home General PSC ta amince da Nadin CP Ibrahim Adamu Bakori matsayin kwamishinan ‘yan...

PSC ta amince da Nadin CP Ibrahim Adamu Bakori matsayin kwamishinan ‘yan sandan Jihar Kano

Hukumar kula da aikin Ƴansanda ta Najeriya (PSC), ta amince da naɗa CP Ibrahim Adamu Bakori, a matsayin sabon kwamishinan ƴansandan jihar Kano.

Shugaban hukumar, DIG Hashimu Argungu mai ritaya ne ya tabbatar da naɗin inda ya nemi sabon kwamishinan da ya tabbatar da an samu zaman lafiya mai ɗorewa a jihar, ta hanyar tunkarar ƙalubalen da ke gabansa wajen tabbatar da an daƙile ƙaruwar aikata laifuka a jihar mai yawan jama’a.

CP Bakori dai zai maye gurbin CP Salman Garba Dogo ne biyo bayan samun ƙarin girma zuwa mataimakin babban sifeto na ƙasa (AIG), kamar yadda sashen Hausa na BBC ya rawaito.

Kafiin naɗin nasa, CP Bakori ya kasance kwamishinan ƴansanda mai kula da sashen binciken kisan kai (Homicide) a shelkwatar ƴansandan ƙasar da ke Abuja.

Jihar Kano dai na fama da matsalolin dabanci da ƙwacen waya da sace-sace, baya ga na baya-bayan nan wato rikicin masarautar Kano da ya janyo al’umma suka sauya tunaninsu kan rundunar ƴansandan jihar.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp