Home General Kwastam ta ƙwace sama da lita 34,000 na fetur da aka yi...

Kwastam ta ƙwace sama da lita 34,000 na fetur da aka yi safararsa a Taraba

Hukumar hana fasa kwauri a Najeriya ta ce jami’anta na Operation Whirlwind sun ƙwace litar man fetur 34,470 wanda aka yi safararsa a jihar Taraba, a ƙoƙari da take yi wajen yaƙi da masu safarar mai

Babban Kwanturola na hukumar ta kwastam, Bashir Adewale ne ya sanar da haka ga manema labarai a Jalingo, inda ya ce sun samu nasarar ce a garin Gembu na karamar hukumar Sardauna a jihar da kuma Kan-Iyaka da ke makwabtaka da ƙasar Kamaru.

Hanyar da ta bi Kan-Iyakar dai ta kasance gungun wuri da aka fi safarar man fetur zuwa waje.

Adewale ya ce sun kuma ƙwace wata babbar mota dakon kaya da aka yi amfani da ita wajen safarar mai ɗin, inda ya ƙara da cewa sun kai samamen ne tare da haɗin gwiwar hukumar kula da sarrafawa da kuma tace man fetur (NMDPRA) da kuma taimakon ofishin mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan tsaro.

“Mun ƙwato jarakuna mai 1,149 – kowane yana ɗauke da lita 30, abin da ya tashi zuwa lita 34,470,” in ji Adewale.

Ya ce masu safarar barazana ne ga tsaron ƙasar kuma ya zama wajibi a kama tare da hukunta su.

Ya yi kira ga mazauna jihar da su bai wa gwamnati haɗin-kai domin tabbatar da ganin cewa an kakkaɓe ɓata-garin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp