Home General APC ta caccaki El’rufai bisa barin Jam’iyyar

APC ta caccaki El’rufai bisa barin Jam’iyyar

Jam’iyyar APC mai mulki a Najeriya ta ce ɗimuwar rashin samun kujerar minista ce har yanzu ke damun tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru El-Rufai.

Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da Jam’iyyar ta fitar a matsayin martani ga kalaman tsohon gwamnan jihar Kaduna Mallam Nasir El-Rufai a hirarsa da BBC Hausa, inda ya ce jam’iyyar ta bar muradun da aka kafa ta akai wanda ya sa shi ficewa daga cikinta zuwa jam’iyyar SDP.

“El Rufa’i ya faɗi ainihin dalilinsa na nuna damuwa, inda a cewarsu saboda bai ji daɗin yadda shugaba Tinubu da gwamnatinsa suka yi mishi ba kan batun rasa kujerar zama minista, kuma domin ya kare mutuncinsa, shi ne yake sukar jam’iyyar da ta kai shi ga nasara a siyasa.” In ji sanarwar.

Jam’iyyar ta ƙara da cewa ƴan Najeriya na da tunani fiye da yadda El Rufa’i ke musu kallo, kuma sun san cewa son kanshi kawai yake yi ba wai tsantsar damuwa kan ƙasar ba ne.

Sanarwar ta kuma jam’iyyar APC ba ta damu da mataki ko kalaman El Rufa’i ba, kuma suna ci gaba da tarbar sabbin miliyoyin mutane masu shiga jam’iyyar a fadin ƙasar waɗanda ke shiga saboda muradun jam’iyyar masu kyau da kuma goya wa shugaba Tinubu baya kan tsare-tsarensa da ke kawowa ƙasar cigaba.

APC ta kuma ce kiran da ya yi wa sauran ƴan adawa su shiga jam’iyyar SDP, ba komai ba ne illa tsantsar yaudara da ƙeta da kuma ƙoƙarin biyan buƙatun kai.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp