Home General Babu tabbacin Zan yi takara a 2027 -Atiku

Babu tabbacin Zan yi takara a 2027 -Atiku

Tsohon mataimakin shugaban Najeriya, Alhaji Atiku Abubakar ya bayyana cewa babu tabbas ko zai tsaya takarar shugabancin ƙasar a zaɓen shekarar 2027.

Atiku ya bayyana hakan ne a wata tattaunawa da kafar talbijin ta Arise, wanda aka saki wani ɓangarenta a ranar Laraba.

An tambayi Atiku game da wanda zai jagoranci haɗakar da ƴan adawar ƙasar ke ƙoƙarin kafawa, sai Atiku ya ce tamkar abin da ya faru ne a lokacin da suka samar da jam’iyyar APC, inda bayan zaɓen fitar da gwani, dukkanin ƴan takarar suka mara wa mutum ɗaya baya, kuma ya yi nasara a babban zaɓen ƙasar.

Lokacin da aka tambaye shi ko zai yi takara, sai Atiku ya ce “ban sani ba, domin ya kamata ne a samar da kafa mai inganci tukuna.”

A makon da ya gabata ne Atiku Abubakar ya bayyana cewa ƴan adawa na ƙasar na tattaunawa domin yin haɗaka a ƙoƙarin tunkarar jam’iyya mai mulki a zaɓen Najeriya na 2027.

Tsohon mataimakin shugaban ƙasar ne ya zo na biyu a zaɓen shugaban ƙasar na 2023, lokacin da Bola Tinubu ya samu nasara.

Sai dai tun bayan kama mulkin Tinubu al’ummar ƙasar na kokawa kan tashin farashin kayan masarufi da kuma tsadar rayuwa.

Masu lura da al’amuran yau da kullum a ƙasar na alaƙanta hakan da matakan da gwamnatin Tinubu ta ɗauka, kamar na cire tallafin man fetur da barin kasuwa ta tantance darajar kuɗin ƙasashen waje, abin da ya taimaka wajen karyewar darajar kuɗin kasar – naira.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp