Home DUNIYA Gwamnonin PDP 11 sun shigar da ƙara don kalubalantar dakatar da Fubara

Gwamnonin PDP 11 sun shigar da ƙara don kalubalantar dakatar da Fubara

Wasu gwamnoni 11 karkashin jam’iyyar PDP, sun shigar da ƙara gaban kotun koli inda suke kalubalantar dakatarwar da shugaba Bola Tinubu ya yi wa zaɓaɓɓen gwamnan jihar Rivers, Siminalayi Fubara.

Ƙarar da gwamnonin suka shigar ranar Talata, na kuma kalubalantar ayyana dokar ta-baci da aka yi a jihar.

Gwamnonin jihohi da suka shigar da ƙarar sun haɗa da Adamawa da Enugu da Osun da Oyo da Bauchi da Akwa Ibom da Plateau da Delta da Taraba da Zamfara da kuma Bayelsa.

A ƙarar da suka shigar, gwamnonin na kuma son kotun kolin ta ayyana cewa ko shugaban ƙasa na da ikon dakatar da zaɓaɓɓen gwamna na jiha.

Sun kuma buƙaci kotun ta yanke hukuncin cewa ko yadda shugaban ƙasa ya ayyana dokar ta-ɓaci a jihar ta Ribas bai saɓa wa kundin tsarin mulki na 1999 ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp