Home General Tinubu zai gana da shugabannin tsaro a Najeriya

Tinubu zai gana da shugabannin tsaro a Najeriya

Rahotanni a Najeriya na nuna cewa, shugaban ƙasar Bola Ahmed Tinubu na shirin yin wata ganawa da hafsoshin tsaron ƙasar kan kashe-kashe a jihohin Filato da Benue da wasu sassan ƙasar.

Ganawar na zuwa ne bayan komawar shugaba Tinubu Najeriyar, bayan kwashe makonni biyu yana ziyarar aiki a Paris, babban birnin Faransa.

Ana sa ran ganawar za ta sake duba ƙarin tashin hankalin da ake samu da kuma matakan magance su.

Hakan na zuwa ne a yayin da gwamnatin ƙasar ke ɗora laifin ƙarin kashe-kashen da ake samu a kan gwamnonin jihohi.

Gwamnatin tarayyar na ɗora alhakin hakan kan rashin sanya kuɗaɗe kamar yadda ya kamata a cibiyoyin tsaron da ke jihohi duk da ɗumbin kuɗaɗen da ake warewa domin yin hakan.

Matsalar tsaro na ci gaba da zama babban ƙalubale ga hukumomin tsaro a ƙasar, lamarin da ke sanadiyyar mutuwar dubban rayuka.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp