Home General Ma’aikatan hukumar NIMET sun janye yajin aiki a Najeriya

Ma’aikatan hukumar NIMET sun janye yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma’aikatan hukumar kula da yanayi ta Najeriya (NIMET) sun sanar da janye yajin aikin da suka fara kwana biyu da suka gabata bayan wata ganawa da suka yi da ministan sufurin ƙasar.

Yajin aikin da ma’aikatan suka kira, ya haifar da cikas a filayen jiragen sama na cikin gida inda fasinjoji da dama suka kasa yin balaguro.

Ma’aikatan sun yi yajin aikin ne saboda rashin ingantacen yanayin aiki, rashin gudanar da ayyukansu ya kawo cikas a zirga-zirgar jiragen sama a fadin ƙasar ranar Alhamis

Ma’aikatan sun nuna damuwa kan rashin aiwatar da sabon tsarin albashi mafi ƙaƙanta, da batun wasu alawus-alawus, da kuma yin watsi da muhimman shirye-shiryen horas da ma’aikatan da dai sauransu.

Amma bayan wata ganawa da ministan sufurin jiragen saman ƙasar Festus Keyamo a Abuja, ƙungiyar ma’aikatan ta yanke shawarar janye yajin aikin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp