Home General Ghana ta kora ƴan Najeriya sama da 200 zuwa gida

Ghana ta kora ƴan Najeriya sama da 200 zuwa gida

Gwamnatin Najeriya ta karbi ƴan asalin ƙasar guda 231 da ƙasar Ghana ta koro, 204 daga cikin su fasa ƙwaurinsu akayi zuwa ƙasar.

Bayanai sun ce mutanen sun sauka a filin sauka da tashin jiragen sama na jihar Lagos, ƙarƙashin tarbar hukumar yaƙi da fasa kwaurin ɗan adam ta ƙasar, da kuma hukumar kula da ƴan Najeriya da ke ƙetare da haɗin gwiwar hukumar yaƙi da yiwa tattalin arzikin ƙasa ta’annati da shirya laifuffuka ta Ghana.

Da yake Magana yayin karɓar mutanen, shugaban hukumar yaƙi da yiwa tattalin arzikin ƙasa ta‘annati da shirya laifuffuka na Ghana Dominic Mensah yace an kama mutanen ne bayan da jami’an tsaro suka bankaɗo wani tuggun shirin aikata laifi a wani rukunin gidaje guda 50 a ƙasar ta Ghana.

Yace tuni jami’an tsaro suka kama mamallakin gidajen don ci gaba da bincike, yayinda ƴan Najeriyar kuma aka yanke shawarar mayar da su gida.

Cikin mutane 204 da aka dawo da su guda 76 yan asalin jihar Edo ne, sai guda sauran da suka fito daga jihohin Anambra, Delta, Bayelsa, Imo, Enugu, Ebonyi da sauran wasu jihohi.

Wani abu mai tada hankali shine yadda 12 daga cikin mutanen ke zaman ƙananan yara ƴan kasa da shekara 18.

Da take mayar da martani kan wannan batu, shugabar hukumar kula da ƴan Najeriya mazauna ƙetare, Abike Dabiri Erewa ta ce ƴan Najeriya na bukatar wayar da kai na musamman game da illar fasa ƙwaurin ɗan adam da kuma shiga wata ƙasa ba bisa ƙa’ida ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp