Home General Tara jam’iyyu barkatai na dagula dimokuradiyya – Ganduje

Tara jam’iyyu barkatai na dagula dimokuradiyya – Ganduje

Shugaban jam’iyyar APC mai mulkin Najeriya, Abdullahi Umar Ganduje ya ce samun jam’iyyu barkatai na dagula tafiyar da gwamnnati a tsarin dimokraɗiyya.

Abdullahi Ganduje ya shaida hakan ne bayan ganawa da Shugaba Tinubu tare da wasu ƴan majalisar PDP da suka koma APC.

Shugaban, ya ce idan duka jam’iyyun siyasar ƙasar za su narke su koma APC, suna maraba da hakan.

”Yanzu idan ka duba ƙasar China tsarin jam’iyya guda suke bi, amma yau ƙasar China jagora ce a duniya wajen samar da ci gaban al’ummarsu”.

Ganduje ya ce idan ƴan Najeriya suka buƙaci komawa tsarin jam’iyyar guda, ba wanda zai yi faɗa da hakan.

Ƴanmajalisar Dattawan Najeriya uku na babbar jam’iyyar hamayya ta PDP daga jihar Kebbi za su sauya sheƙa zuwa jam’iyyar APC mai mulki, kamar yadda shugaban jam’iyyar APC na ƙasa ya tabbatar.

”Sanatocin jam’iyyar PDP daga jihar Kebbi a yau sun tabbatar wa shugaban ƙasa cewa sun fice daga jam’iyyarsu ta PDP tare da dawo jam’iyarmu ta APC”, in ji Ganduje.

Abdullahi Ganduje ya ce sanatocin uku za su bayyana wa majalisar dattawa matsayar tasu a mako mai zuwa kamar yadda kundin tsarin ƙasar ya tanadar.

Sanatocin uku sun haɗa da Sanata Adamu Aliero da Sanata Yahaya Abubakar Abdullahi da kuma Sanata Garba Maidoki.

A baya-bayan nan batun sauya sheƙa tsakanin manyan ƴansiyasa na ci gaba da ɗaukar hankali a ƙasar, bayan da wasu jiga-jigan jam’iyun hamayya ke komawa APC mai mulki.

Ko a makonnin baya ma gwamnan jihar Delta da tsohon gwamnan jihar, Ifeanyi Okowa – wanda shi ne ya yi wa PDP takarar mataimakin shugaban ƙasa a zaɓen 2023 – suka sanar da komawa APC.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp