Home General ‘Yanbindiga sun sace mutum 117 da hallaka wasu tara a Jihar Kebbi

‘Yanbindiga sun sace mutum 117 da hallaka wasu tara a Jihar Kebbi

Rahotannin daga Nijeriya na bayyana cewa wasu ‘yanbindiga sun hallaka akalla mutane tara sannan kuma suka yi awon-gaba da wasu magidanta 117, a garin Danmuntari da ke yankin Danko-Wasagu a jihar Kebbi da ke arewa maso yammacin kasar.

Wasu mazauna garin da suka tsira daga harin sun tabbatar wa da BBC, cewa lamarin ya faru ne a yammacin ranar Talata, 27 ga watan Mayun, 2025, lokacin da ‘yanbindigan su ka yi wa garin kofar-rago.

Daga cikin wadanda barayin dajin suka kashe har da wata mata mai jego da jaririnta, inda suka harbe su tare da sauran jama’ar da suka hallaka ta hanyar harbin kan-mai-uwa-da-wabi a lokacin da suka shiga garin, kamar yadda shedun suka yi bayani.

”Da la’asar barayin suka kewaye garin suka dinga harbe-harbe wanda hakan ya sa dole mutanen garin suka watse suka cimma na kashewa, suka kashe mutum tara,”in ji daya daga cikin mutanen garin.

Ya kara da cewa, ”Abin ban tausayi akwai mace daya da ba ta wuce sati biyu da haihuwa ba suka kashe ta da ita da jaririnta.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp