Home General Rayuwar ƴan Najeriya na ƙara inganta – Tinubu

Rayuwar ƴan Najeriya na ƙara inganta – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu ya ce Najeriya ta kama hanyar inganta kuma lokacin matsi ya wuce.

A jawabinsa na cika shekara biyu da karɓar ragamar mulki, Tinubu ya amince cewa tsare-tsarensa na kawo gyara sun janyo matsi kuma bai raina haƙuri da kuma uzurin da ƴan Najeriya suka nuna masa ba.

“A yau ina alfahari cewa sauye-sauyen mu a fannin tattalin arziki suna aiki. Mun kama hanyar samar da ƙasa mai ƙarfin tatalin arziki,” in ji shi.

A ranar da aka rantsar da shi a cikin watan Mayun 2023, shugaba Tinubu ya sanar da janye tallafin man fetur da aka daɗe ana cece ku-ce a kai, lamarin da ya janyo tsadar rayuwa a ƙasar.

Tinubu ya ce: “Duk da tsadar rayuwa da muka faɗa, mun samu ci gaba sosai. Hauhawar farashi ta fara raguwa musamman a kan farashin shinkafa da sauran kayayyaki.”

Alƙaluman da hukumomi suka fitar sun nuna cewa hauhawar farashi ya ƙaru zuwa kashi 24 cikin ɗari a watan da ya gabata, idan aka alaƙanta da kashi 22 da ake ciki a lokacin da Tinubu ya karɓi mulki.

A haka ma an samu raguwa ne idan aka kwatanta da kashi 34 da aka samu a shekarar da ta gabata, lamarin da ya janyo zanga-zanga a sassan ƙasar har ta kai ga asarar rayuka.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp