Home General Najeriya ce kan gaba a yawan fitar da man fetur a Afirka...

Najeriya ce kan gaba a yawan fitar da man fetur a Afirka cikin watan Mayu – OPEC

Ƙungiyar ƙasashe masu arzikin man fetur ta OPEC ta ce duk da raguwar fitar da mai da aka samu a Najeriya, har yanzu ƙasar ce ta fi kowace ƙasa yawa fitar da mai a Afirka.

A cikin rahotonta na wata-wata da ta fitar a ranar Litinin, ƙungiyar ta OPEC ta ce fitar da ɗanyen mai daga Najeriya ya ragu zuwa ganga miliyan 1.45 a kullum a watan Mayu — daga ganga miliyan 1.48 da aka samu a watan da ya gabata.

Rahoton ya bayyana cewa duk da wannan raguwar, Najeriya ta ci gaba da zama ƙasa kan gaba a yawan fitar da danyen mai a nahiyar Afirka, inda ta zarce ƙasashen Libya da Aljeriya da Kongo.

OPEC ta ce ta samo waɗannan alƙaluma ne daga bayanan da ƙasashe suka bayar kai tsaye.

OPEC ta ƙara da cewa alƙaluman da aka samu ya nuna cewa Najeriya ta fitar da ganga miliyan 1.54 a kullum a watan Mayu, wanda ya ƙaru daga ganga miliyan 1.52 da aka samu a watan Afrilu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp