Home General Mutane 5 sun gamu da ajalinsu sakamakon fashewar wani abu a Kano

Mutane 5 sun gamu da ajalinsu sakamakon fashewar wani abu a Kano

Aƙalla mutane biyar aka tabbatar  sun mutu, kana wasu 15 suka jikkata sakamakon fashewar wani abu da ake zargin bam ne a Jihar Kano da ke arewa maso yammacin Najeriya.

Rundunar ƴansandan jihar, ta bakin kwamishinanta, Ibrahim Adamu Bakori, wadda ta tabbatar da aukuwar lamarin, ta ce ya faru ne akan bypass na Mariri dake yammacin birnin Kano.

Rahotanni sun ce jami’an ƴansanda da na hukumar agajin gaggawa sun garzayar wurin da aka samu fashewar domin kai ɗauki, a yayin da lamarin ya haddasa ruɗani da firgici a zukatan al’ummar yankin.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Kano, Ibrahim Adamu Bakori, ya ce fashewar na iya kasancewa bam ɗin da sojoji suke jigilarsa ne wanda aka yi sakaci ya fashe.

Binciken farko-farko ya nuna cewa abin fashewar na cikin wata babbar mota ce, wadda ta ɗauko kaya, mallakain wasu masu sana’ar gwangwan, kuma take kan hanyar zuwa Jihar Yobe.

Rundunar ƴansandan Kanon ta ce ta gani wasu ƙakkrin abubuwan fashewa da ba su kai ga tashi ba a inda lamarin ya faru, kuma  tana  cigaba da bincike akan yadda aka samo su.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp