Home General Rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da kashe jami’anta a Neja

Rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da kashe jami’anta a Neja

Rundunar Sojin Najeriya ta tabbatar da mutuwar wasu daga cikin jami’anta sakamakon hare-haren da wasu ƴan bindiga suka kai kan sansanonin soji da ke jahohin Neja da Kaduna.

Rundunar ta bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ta wallafa a shafin sada zumunta na X.

A cewar sanarwar, hare-haren sun faru ne a ranar Litinin, 24 ga Yuni, 2025, a sansanonin sojin da ke Kwanar Dutse Mairiga da Boka a Jihar Neja, da kuma Aungwan Turai da ke ƙaramar hukumar Chikun a Jihar Kaduna.

Rahotanni sun ce ƴan bindigar sun kai hari ta ɓangarori uku a lokaci guda, lamarin da ya sa dakarun soji suka mayar da martani cikin gaggawa.

A yayin musayar wuta ne rundunar soji ta tura dakarun ƙasa da na sama don fatattakar maharan, kamar yadda sanarwar ta bayyana.

Rundunar ta ce an kashe ƴan bindiga da dama yayin gumurzun da ya ɗauki sa’o’i.

“Sai dai kuma, an kashe mana wasu jami’ai yayin musayar wuta da ƴan bindigar.”, in ji sanarwar.

Baya ga haka, rundunar ta kuma ce wasu sojoji huɗu sun jikkata sakamakon harbin bindiga kuma suna samun kulawar a asibiti.

Rundunar sojin ta bayyana waɗanda suka mutu a matsayin “jarumai” da suka tsaya tsayin daka wajen kare matsayinsu da mutuncin ƙasa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp