Home Labarai Yadda Jami’an tsaro suka kama ni -Danbello

Yadda Jami’an tsaro suka kama ni -Danbello

Rahotannin sun tabbatar da cewa jami’an tsaro a Nigeria sun kama Mai Wasan barkwancinan a shafukan sada zumunta Dr. Bello Habib Galadanci wanda aka fi Sani da Danbello.

Danbello dai ya jima ya yin wasanni barkwanci inda a ciki yake nuna yadda Shugabanni a Nijeriya suka Gaza yiwa talakawan Kasar abubuwan da suka dace.

An dai kama Danbello ne a filin jirgin sama na Malam Aminu Kano dake Kano , Jim kadan bayan saukarsa daga jirgin sama .

Dama dai Danbello yana zaune ne a Kasar China inda daga chan yake yin duk abun da yake yi .

Ana zargin Jami’an tsaron da suka kama Danbellon sun zo ne daga Abuja.

Sai dai duk da cewa ba a bayyana dililin kama Danbello ba, Amma mintoci kadan bayan kama shin kuma aka sake shi .

A wata hirarsa da manema labarai Danbello ya ce ” Bayan sakkowarmu daga jirgi sai wasu mutane masu kama da Jami’an tsaro suka karbi Fasfo dina da sauran takarduna , kuma suka ce In shiga wata mota”.

” Ana haka sai ga Barr. Abba Hakima nan sai akai Dan yi waya sannan akai dogon turanci bayan awa daya sai suka sallameni, Amma dama ban yi mamakin kamani ba, don dama da Shirin hakan na zo.

Tuni dai Danbello yana cikin Iyalansa bayan sakinsa da Jami’an tsaron suka yi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp