Home Labarai NAFDAC ta gano gidan ajiye sinadaran haɗa abubuwa masu fashewa a Kano

NAFDAC ta gano gidan ajiye sinadaran haɗa abubuwa masu fashewa a Kano

Hukumar kula da ingancin abinci da magunguna ta ƙasa (NAFDAC) ta gano wani babban gidan ajiya a Kano da ke cike da sinadarai masu haɗari da ake amfani da su wajen haɗa abubuwa masu fashewa, ciki har da sinadarin sulphuric da nitric acid kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

cewar hukumar, an gano lita 60,000 na sulphuric acid da kuma lita 28,560 na nitric acid da kuma jarkoki da suka kai 330 da aka riga aka fitar da sinadaran cikinsu ba tare da sanin inda aka kai su ba a cikin gidan.

“Abin da muka gani a nan ya girgiza mu. Ban taɓa ganin adadin waɗannan sinadarai masu haɗari a wuri guda ba,” in ji Farfesa Adeyeye.

Hukumar ta ce ba a samu wandan yake da gidan ajiyar ba a lokacin da aka isa wurin, amma an kama wani ma’aikacin da ke kula da wurin, kuma ana ci gaba da bincike don gano wanda yake da wurin da kuma inda ya samo sinadaran da kuma inda yake kai su.

NAFDAC ta bayyana cewa sinadaran na cikin jerin kayan da ke da haɗari sosai ga mutane saboda haka sai da izini daga ofishin mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro kafin a shigo da su ƙasar.

Hukumar ta kuma tabbatar da cewa za ta lalata sinadaran bisa ka’idojin da suka dace don kare lafiyar jama’a, sannan za ta tabbatar da cewa an gurfanar da wanda ya mallaki sinadaran a gaban shari’a.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp