Home Labarai Hare-haren ƴan bindiga a jihar Filato na ci gaba da lakume rayuka

Hare-haren ƴan bindiga a jihar Filato na ci gaba da lakume rayuka

Akalla mutum 14 da wani ɗan sanda na MOPOL ne suka mutu a hare-hare biyu da wasu ‘yan bindiga suka kai a ƙaramar hukumar Bokkos da ke Jihar Filato a ranar Alhamis, 24 ga Yuli, 2025.

Rahotanni sun ce an kai ɗaya daga cikin hare-haren ne da misalin ƙarfe 4 na yamma, yayin da mutanen da lamarin ya shafa mafi yawansu daga ƙauyen Chirang ke dawowa daga kasuwar Bokkos zuwa ƙauyen Mangor.

Shugaban masu sa ido kan zaman lafiya na ƙaramar hukumar Bokkos, Kefas Mallai ne ya tabbatar da faruwar lamarin ga jaridar Punch inda ya ce mutane 14 ne suka mutu, yayin da wasu uku kuma suka jikkata.

A cewar Mallai, kafin wannan harin, wasu ‘yan bindiga sun harbe wani ɗan sandan MOPOL a wani shingen bincike da ke hanyar Richa a safiyar ranar.

Shugaban ƙaramar hukumar Bokkos, Amalau Amalau, ya bayyana lamarin a matsayin “taƙaici da ke buƙatar ɗaukar matakin gaggawa,” yana mai cewa an riga an kai gawarwaki da waɗanda suka jikkata zuwa Asibitin Koyarwa na Jami’ar Jos.

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, Alabo Alfred, bai samu damar bayyana komai ba a lokacin da aka nemi jin ta bakinsa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp