Home Labarai Yadda Hukumar KAROTA ta karbi koken direbobin mota a jihar Kano

Yadda Hukumar KAROTA ta karbi koken direbobin mota a jihar Kano

Wasu daga cikin Direbobin Bus a Jihar Kano sun koka bisa yadda Jami’an Hukumar Karota ke matsa mutsu Jahar.

Wannan na cikin wata sanarwa da Mai Magana da yawun hukumar ta KAROTA Abubakar Ibrahim Sharada ya fitar ya kuma aikewa manema labarai a jihar Kano.

Direbobin sun kai Koken ne a shalkwatar Hukumar ta lura da zirga-zirgar ababawan ta jihar Kano da nufin a duba domin magance masu matsalar.

Jagoran ayarin Kungiyar Matasan Direbobi ta Garin Kunya dake yankin Karamar Hukumar Minjibir, Mumfadalu Bukar Sakatare Ya koka bisa yadda jami’an Hukumar Karota Ke yawan kama Motocin Bus a duk lokacin da suka fito don gudanar da sana’ar su.

“Duk da cewar yanzu Direbobin a Daidaita Sahu sun Kwace mana akasarin Fasinjojin da mu direbobin Bus muke dauka hakan bata sanya Jami’an Karota sun saurara mana ba wajen kame Motocin mu”, inji Mumfadalu Sakatare.

“Tun da gwamatin Jahar Kano mai ci yanzu ta dagawa Direbobin A Daidaita Sahu kafa, to muma Direbobin Bus mun cancanci wani karamci na Gwamnati wajen karbar Kudaden shiga.” a cewar Jagoran Direbobin na Matasan Kunya.

Yana magane kan Kudaden Sticker wanda ya ce akan haka Jami’an Hukumar KAROTA Ke yawan kame motocin su.

A jawabin sa, Shugaban Hukumar KAROTA, Hon Faisal Mahmud Kabir ya yabawa Kungiyar Matasan Direbobi ta Garin Kunya bisa Kawo wannan koke da suka yi, a madadin sauran Direbobin Bus.

Manajan Daraktan wanda Daraktan kula da harkokin Kudaden shiga na Hukumar KAROTA, Alh Nura Ahmad Diso Ya wakilta yace abinda direbobin suka kawo koke akan sa hurumi ne na Gwamnatin Tarayya, don haka ya shawar ce su dasu miƙa Koken zuwa Hukumar tattara Kudaden Haraji ta Jahar Kano don magan ce al’amarin.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp