Home Labarai Ambaliyar ruwa ta lalata gidaje tare da kashe mutane 23 da a...

Ambaliyar ruwa ta lalata gidaje tare da kashe mutane 23 da a birnin Yola

Rahotannin daga Najeriya na bayyana cewa, ruwan sama kamar da bakin kwarya da aka yi babu kakkautawa ya haifar da ambaliya a ƙananan hukumomin Yola ta Arewa da Yola ta Kudu na jihar Adamawa, inda rahotanni suka ce an samu rasa rayukan aƙalla mutum 23 da rugujewar gidaje.

Ruwan sama kamar kamar da bakin kwarya, wanda aka fara tun kafin wayewar gari kuma ya ci gaba har zuwa safiyar Lahadi, ya yi barna sosai ga al’ummomin yankin.

unguwannin da lamarin ya fi shafa sun hada da Yola Bye Pass da Sabon Pegi da Yolde Pate da Modire, saboda yadda gidaje suka ruguje, tare da lalata filayen noma da hanyoyin mota, lamarin da ya hana zirga-zirgar mutane da ababen hawa.

Rahotanni na cewa mutane da dama sun mutu, yayin da ƙanan yara da dama suka bace, inda har yanzu ake ci gaba da aikin ceto.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp