Home DUNIYA Majalisar Dokokin Kano ta Dakatar da Ciyaman din Rano

Majalisar Dokokin Kano ta Dakatar da Ciyaman din Rano

Majalisar jihar Kano
Majalisar jihar Kano

Majalisar dokokin jihar Kano ta dakatar da shugaban karamar hukumar Rano Alhaji Naziru Ya’u na tsawon watanni uku sakamakon rashin Iya tafiyar da mulki da karya dokokin aiki tare da umartar sa ya mika aiki ga mataimakin sa.

Majalisar ta dauki wannan matakin ne yayin zaman da ta gudanar a Wannan Rana ta Laraba.

Rahotanni dai sun nuna cewa ana zargin Shugaban karamar hukumar da aka dakatar da sayar da takin zamani ko karkatar da shi wanda gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya rabawa kananan hukumomin kano a watan Yulin da ya gabata.

Ko wacce karamar hukuma ta samu tirela uku na takin zamanin mai dauke da buhu 600 ko wacce mota

Haka kuma Majalisar ta yi karatu na daya akan kudirin dokar kwarya kwaryar kasafin kudi na wannan shekarar da gwamna Abba Kabir Yusuf ya aike mata wanda yakai fiye da naira biliyan dari da sittin da tara.

Akawun majalisar Alhaji Bashir Idris Diso shine yayi karatun a yayin zaman majalissar na yau laraba.

Zaman majalissar Wanda shugaban ta Alhaji Jibril Isma’il Falgore ya jagoranta ya amince Gwamna Abba Kabir Yusuf ya nada Alhaji Sa’id Yahaya a matsayin shugaban hukumar karbar korafi da hana cin hanci da rashawa ta jihar Kano.

Hakan ya biyo bayan rahoton da shugaban kwamitin karbar kirafi na majalissar kuma dan Majalissa mai wakiltar karamar hukumar Dala Alhaji Lawan Hussaini Chediyar Yan Gurasa ya gabatar.

Ya ce Alhaji Sa’id Yahaya ya cika dukkanin Ka’idojin da doka ta tanadar kafin nada mutum a matsayin shugaban hukumar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp