Home Labarai PDP za ta ƙaddamar da kwamitocin zartaswa na shiyoyi

PDP za ta ƙaddamar da kwamitocin zartaswa na shiyoyi

Babbar jam’iyyar adawa a Najeriya PDP na shirin kaddamar da kwamitocin zartaswa na shiyoyi da kuma kwamitin tsara zaɓen shugaban ƙasa na jam’iyar na shekarar 2027 a ranar Alhamis a Abuja.

Wannan na zuwa ne yayin da ake samun rabuwar kawuna tsakanin mambobin kwamitin zartaswa na ƙasa na jam’iyar wato NEC kan yunƙurin dawo da tsohon shugaban ƙasa Goodluck Jonathan da kuma ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour a 2023, Peter Obi, cikin jam’iyyar.

Wasu daga cikin shugabannin PDP na ganin cewa Jonathan ya bar jam’iyyar a lokaci mai muhimmanci, yayin da Obi kuma ya yi sauya sheƙa zuwa Labour, lamarin da ya rage wa jam’iyyar damar samun nasara a zaɓen 2023.

Sai dai wasu mambobin kwamitin zartaswar sun yi maraba da wannan yunƙuri, suna cewa PDP na da isassun jiga-jigai masu kwarewa waɗanda za su iya wakiltar jam’iyyar a zaɓen 2027.

Rahotanni sun tabbatar da cewa jam’iyyar ba ta kai ga tuntuɓar Jonathan da Obi a hukumance ba, sai dai wasu mutane ne daban-daban ke yin hakan a madadinta.

Kakakin jam’iyyar PDP na ƙasa, Debo Ologunagba, ya ce ƙaddamar da kwamitin zartarwar zai gudana ne a ranar Alhamis, tare da jaddada cewa jam’iyyar na da wadatattun masu neman takarar shugabanci a cikinta.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp