Home General kotu ta dakatar da asusun banki huɗu na Mele Kyari

kotu ta dakatar da asusun banki huɗu na Mele Kyari

Wata Babbar Kotun Tarayya a Abuja babban birnin Najeriya ta bayar da umarnin dakatar da wasu asusan da ke da alaƙa da tsohon shugaban kamfanin mai na NNPCL Mele Kyari.

Kotun ta bayar da umarnin dakatar da asusan na bankin Jaiz saboda zargin zamba da kuma halasta kuɗin haram.

Mai Shari’a Emeka Nwite ne ya bayar da umarni bayan wani lauyan hukumar EFCC mai yaƙi da cin hanci, Ogechi Ujam, ya nemi kotun ta dakatar da amfani da asusan har zuwa lokacin da hukumar za ta kammala bincike a kansu.

“Na saurari mai ƙorafi kuma na duba takardun ƙorafin da suka shigar masu ɗauke da hujjoji da bayanai. Na lura cewa buƙatarsu ta cancanci a amince da ita,” kamar yadda alƙalin ya bayyana.

Mai Shari’a Nwite ya ɗage sauraron batun har zuwa ranar 23 ga watan Satumba domin ganin rahoton binicken.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp