Home Labarai Gwamnatin Nijeriya ta rufe wurin hakar zinare a Abuja

Gwamnatin Nijeriya ta rufe wurin hakar zinare a Abuja

Gwamnatin tarayya ta bayar da umarnin rufe wurin hakar maádanai ba bisa kaída ba a Gwagwalada dake birnin tarayya Abuja, domin dakile hadarin aukuwar matsalar sauyin yanayi

Ministan ma’adanai na tarayyar Nijeriya, Dele Alake, ne ya bayar da umarni rufe wurin biyo bayan samun rahotanni na sake farfadowar ayyukan hakar zinare ba bisa ka’ída ba a yankin.

ta cikin wata sanarwa da Jaridar Economic Confidencial ta samu, wadda tace jami’an hukumar sun gudanar da wani sumame ranar 16 ga watan Agusta a yankin unguwar District 2 Extension, in da suka sami nasarar kama mutum 16 da ake zargi.

Ta cikin sanarwar mataimaki na musamman kan harkokin yada labarai ga minstan Segun Tomori ya ce wannan ya biyo bayan wata zinariya da aka samu a unguwar yayin da ake hakar masai a kusa da wani gida a yankin.

ya ce dakarun lura da hakar ma’adanai, karkashin Jagorancin John Atta Onoja, sun kafa shingen bincike na tsahon sa’o’i 24 a wuraren da abin ya shafa, har sai na kammala bincike a wuri.

takardar ta ambaci Alake na jan hankalin mazauna yankin game da hadarin gurbatar muhalli ga lafiyar jama’a da ke tattare da irin wadannan ayyuka, yana mai shawartarsu da su guji shiga wuraren da abin ya shafa har sai an kammala aikin tsaftace muhalli da tabbatar da doka.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp