Home General ASUU na barazanar shiga yajin aiki a jami’o’in Najeriya

ASUU na barazanar shiga yajin aiki a jami’o’in Najeriya

Ƙungiyar malaman jami’o’i ta Najeriya (ASUU) ta bayyana cewa dukkan jami’o’in gwamnati kusan 150 da ke ƙarƙashin kulawar ta na iya shiga yajin aiki, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

Wannan lamari ya biyo bayan da gwamnati ta musanta cewa ta rattaba hannu kan wata yarjejeniya da ASUU, inda ta bayyana takardun da ƙungiyar ke magana a kansu a matsayin shawarwari ne kawai.

Daga ranar Litinin din wannan makon, rassan ASUU daban-daban sun yi kira ga gwamnatin tarayya da ta aiwatar da yarjejeniyar da aka cimma da ƙungiyar ko kuma a fuskanci yajin aikin da zai shafi ɗalibai kusan miliyan biyu a faɗin ƙasar.

Manyan matsalolin sun haɗa da rashin biyan albashin watanni uku da rabi da aka hana da rashin biyan cikon kuɗin albashi na ƙarin matsayi da rashin sakin kuɗaɗen inganta jami’o’i da sauya sunan Jami’ar Maiduguri, da batun kudin ritaya ga malaman jami’a.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp