Home General Kofa ya sanar da ficewarsa da ga NNPP

Kofa ya sanar da ficewarsa da ga NNPP

Dan Majalisa Mai wakiltar kananan hukumomin Kiru/Bebeji a zauren majalisar wakilan Nijeriya Abdulmumin Jibril Kofa ya sanar ficewarsa daga Jam’iyyar NNPP.

ta cikin wata sanarwa da jaridar Politics Digest ta samu kofa ya dangwarar da shahadar Jam’iyyar ne bayan abinda ya kira sharin adalci da shugabancinta yayi masa.

Wannan dai na zuwa ne biyo bayan ikirarin jam’iyyar na korar sa daga cikinta bisa abinda ta kira karya dokokinta tare da gaza biyanta wasu kudade da ya kamata ya biya na hakkoki.

daga cikin abubuwan da Jam’iyyar ta yi wukar kugu da su na korar Kofa akwai wata hira da ya yi a ‘yan tsakaninnan da yake yabon shugaban kasa Tinubu wanda ba Dan Jam’iyyar sa bane, wanda ta ce hakan ya saba dokokinta.

Sai dai kuma Kofa ta cikin sanarwar ficewarsa daga Jam’iyyar yace matakin da Jam’iyyar ta dauka akan sa ya zo masa a matsayin ba zata, kasancewar yasan bai karya wata dokar Jam’iyya.

“ganawar da nayi da manema labarai cikin harshen hausa da turanci, ban fadi wasu kalamai da ya kamata jam’iyyar ta yi min wannan mummunan hukunci ba,” yace hasalima kalamansa sun bi sahun dokoki da tsarin jam’iyyar ya tanadar wanda yake kara dabbaka damar fadin ALbarkacin baka.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp