Home Labarai Sojojin Nijeriya sun hallaka ‘yan ta’adda 6 a jihar Zamfara

Sojojin Nijeriya sun hallaka ‘yan ta’adda 6 a jihar Zamfara

Dakarun Operation FANSAN YAMMA sun sami nasarar hallaka ‘yan bindiga 6 a jihar Zamfara dake arewa maso yammacin Nijeriya, yayin da sojoji uku suka rasa rayukansu a harin kamar yadda PRNigeria ta gano

Wata majiya ta shaidawa mai sharhin kan harkokin tsaro Zagazola Makama cewa lamarin ya auku ne a karamar hukumar Bugudu yayin da dakarun Operation Base (FOB) da ke lilo suka fuskancin ruwan wuta a lokacin da su ke kokarin fitar da wata mota da ta makale a Fegin Rama.

An kara girke dakarun kawo dauki amma suka sake fuskantar harin kwantan bauna nan suka yi wata musayar wuta da ‘yan ta’addan

Majiyar ta tabbatar da cewa dakarun sojin sun ci karfin maharan, in da suka hallaka 6 daga cikin su, suka kuma tilastawa da dama guduwa domin cira da rayukansu, sai dai kuma sojoji 3 sun mutu a kokarin su na kare kasar daga hadarin ‘yan ta’adda.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp