Home General DSS ta gurfanar da Sowore a kotu kan zargin ‘aibata’ Tinubu a...

DSS ta gurfanar da Sowore a kotu kan zargin ‘aibata’ Tinubu a shafin X

Hukumar tsaro ta DSS a Najeriya ta gurfanar da tsohon ɗan takarar shugaban ƙasar Omoyele Sowore a gaban wata babbar kotun tarayya da ke Abuja a yau, Talata, bisa zargin shi da aibata shugaba Bola Tinubu a shafinsa na X.

Hakazalika, DSS ta gurfanar da manyan kamfanonin sada zumunta na X da Meta a matsayin waɗanda ake ƙara.

Hukumar ta ce waɗannan kamfanoni sun ƙi goge abin da suka kira kalaman ƙarya da cin mutunci da aibata shugaba Tinubu da Sowore ya wallafa a shafinsa na sada zumunta.

Tun a ranar 6 ga watan Satumban 2025 ne DSS ta sanar da cewa ta nemi a rufe ko a dakatar da shafin Sowore a dandalin X bisa zargin cewa yana yaɗa kalamai da za su iya haifar da rikici da barazana ga tsaron ƙasa.

Hukumar ta ce ta ɗauki wannan mataki ne domin kare martabar shugabanci da kuma kare ƙasar daga mummunar tasirin yaɗa labaran ƙarya.

Hukumar ta bayyana cewa kalaman kai tsaye a kan Tinubu barazana ce ga tsaron ƙasar inda ta yi kira ga kamfanin X da ya goge tare da gaggauta rufe ko dakatar da shafin Sowore.

Amma kuma har yanzu X bai rufe shafin nasa ba inda DSS ta zargi kamfanin da rashin bin umarninta dalilin da ya sa ta gurfanar da kamfanin a gaban kotu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp