Home Labarai Gwamnan Enugu ya koma APC bayan ficewa daga PDP

Gwamnan Enugu ya koma APC bayan ficewa daga PDP

Gwamnan jihar Enugu, Peter Mbah ya fice daga jam’iyyarsa ta PDP tare da komawa APC mai mulkin Najeriya.

Mista Mbah ya bayyana haka ne a wani taron manema labarai da ya shirya a fadar gwamnanatin jihar da ke birnin Enugu.

“Bayan dogon lokaci da muka ɗauka muna nazari, a yau mun yanke shawarar ficewa daga PDP tare da komawa APC,” kamar yadda gwamnan ya bayyana.

Mbah ya ce ya koma APC ne saboda kyawawan manufofin jam’iyyar da ayyukan ci gaba da take samarwa a Najeriya da ma jiharsa ta Enugu.

Gwamnan ya ce yana da ƙwarin gwiwar cewa komawarsa APC za ta samar wa jihar ƙarin damarmaki da ci gaba.

Taron ya samu halartar manyan ƴansiyasar jihar da suka haɗa da mataimakin gwamnan jihar, Barr Ifeanyi Ossai da tsoffin gwamnonin jihar, Sullivan Chime da Rt Hon. ifeanyi Ugwuanyi,da Tsohon Shugaban Majalisar Dattawan Najeriya, Chief Ken Nnamani, da tsoffin ƴanmajalisar tarayya daga jihar da kuma masu ci, da shugaban majalisar dokokin jihar da shugaban jam’iyyar APC na jihar, da sauran muƙarraban gwamnatinsa, kamar yadda mataimaki na musamman ga gwamnan kan kafofin yaɗa labarai, Dan Nwomeh ya wallafa a shafinsa na X.

Dama dai tun jiya wasu daga cikin kwamishinonin gwamnan suka fice daga PDP tare da komawa APC.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp