Home Labarai Za ayi bincike kan masu laifin da Tinubu ya yiwa Afuwa

Za ayi bincike kan masu laifin da Tinubu ya yiwa Afuwa

Babban ministan shari’a na Najeriya kuma babban lauyan gwamnati, Lateef Fagbemi, ya bayar da umarni ga hukumomi da dama su gudanar da bincike kan jerin sunayen masu laifin da shugaban ƙasar Bola Tinubu ya yi wa afuwa, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

Fagbemi ya bayyana hakan ne a yayin taron Majalisar mahukunta da aka gudanar a ranar Alhamis, 9 ga Oktoba, 2025. in da ya ce hukumomin da za su gudanar da wannan binciken sun haɗa da hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa (EFCC), hukumar yaƙi da sha da fataucin miyagun ƙwayoyi (NDLEA), da kuma Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya.

Ana hasashen cewa binciken zai iya kai ga cire fiye da rabin sunayen mutanen da aka yi wa afuwa.

Shugaba Bola Ahmed Tinubu dai na jira a mika masa jerin sunayen da aka tantance domin ya sanya hannu na karshe, a yunkurin tabbatar da cewa duk wanda zai amfana daga afuwar ya cancanta.

Tinubu dai ya yi amfani da ikon da ƙundin tsarin mulki ya ba shi wajen yi wa mutum 175 da aka samu da laifuka daban-daban afuwa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp