Home Labarai Babu wasu bayanan an yi wa masu bin wani addini kisan ƙare...

Babu wasu bayanan an yi wa masu bin wani addini kisan ƙare dangi – Sultan

Mai alfarma Sarkin Musulmi, Muhammad Sa’ad Abubakar III, ya bayyana cewa babu wasu bayanan da ke nuna cewa an yi wa masu bin wani addini ko Kirista ko Musulmi kisan ƙare dangi a Najeriya.

Sarkin ya faɗi hakan ne a yayin buɗe taron Majalisar Sarakunan Arewa a Birnin Kebbi, 2025.

Sarkin ya ce, “Babu yadda za a kashe wani mutum, ko Musulmi ko Kirista, ba tare da sanin sarakuna ko shugabannin al’ummar da wannan mutumin ya fito ba.”

Ya kuma ƙalubalanci kowa, a cikin gida ko waje, da su kawo hujja ta gaske kan wani kisan ƙare dangi a Najeriya.”

Sultan Sa’ad ya gargadi jama’a da kada su gaskata duk abin da suka gani ko karanta a kafafen sada zumunta, yana mai cewa yawancin bayanan da ake yaɗawa ba gaskiya bane.

“Yawancin abin da aka wallafa a kafafen sada zumunta ba gaskiya bane. Dole mutane su tabbatar da sahihancin bayani kafin su ɗauke shi a matsayin gaskiya,” in ji shi.

Sarkin ya bukaci Gwamnatin Tarayya da ta hanzarta tsara dokoki da za su kula da ayyukan masu amfani da kafafen sada zumunta domin rage yaɗa labaran ƙarya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp