Home General Gwamnatin Najeriya ta dakatar da fara karɓar harajin man fetur

Gwamnatin Najeriya ta dakatar da fara karɓar harajin man fetur

Hukumar kula da harkokin man fetur a Najeriya ta ce ta dakatar da shirin fara karɓar harajin kashi 15 cikin 100 kan albarkatun man fetur ɗin da ake shigarwa ƙasar daga ƙasashen waje.

Mai magana da yawun hukumar Nigerian Midstream and Downstream Petroleum Regulatory Authority (NMDPRA), George Ene-Ita, ya faɗa cikin wata sanarwa a ranar Alhamis cewa ya kamata ‘yan Najeriya su daina fargaba.

A ranar 29 ga watan Oktoba ne Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya amince da saka harajin kan man fetur da dizel, wanda zai ƙara farashin man da ake saukewa a defo-defo, kuma ɗaya daga cikin manufarta shi ne ƙarfafa matatun mai na cikin gida.

Gwamnatin Najeriya ta tsara fara aiki da harajin daga ranar 21 ga watan Nuwamban nan, kafin matakin da NMDPRA ta sanar.

Duk da manufar ƙarfafa matatun mai na cikin gida da harajin zai yi, zai kuma iya jawo hauhawar farashin a gidajen mai kasancewar har yanzu Najeriya na shigar da fetur mai yawa daga ƙasashen waje.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp