Home Labarai Ma’aikatan lantarki sun yi barazanar katse wuta a faɗin Najeriya

Ma’aikatan lantarki sun yi barazanar katse wuta a faɗin Najeriya

Ƙungiyar ma’aikatan lantarki ta Najeriya (NUEE) ta yi barazanar katse wuta a faɗin ƙasar, sakamakon zargin da take yi na cewa an kai wa ma’aikatan kamfanin rarraba lantarki na ƙasar hari.

Cikin wata sanarwa da muƙaddashin babban sakataren ƙungiyar, Dominic Igwebike ya fitar, ya ce hakan ya zama wajibi ne bayan zargin wasu ƴansanda da ke aiki bisa umurnin gwamnatin jiha, sun yi wa ma’aikatan da ke aiki a cibiyar lantarki ta Egbu da ke Jihar Imo duka, da yi musu barazana da bindiga da kuma garkuwa da wasu.

A cewar sa ƴan sandan sun shiga cibiyar ne da ƙarfin tsiya, tare da lalata kayayyakin aiki da dakatar da ayyukan da ake gudanarwa, kamar yadda kafar talibijin ta channels ta ruwaito.

A cewar sanarwar, ƙungiyar ta riga ta bai wa mambobinta umurnin katse samar da lantarki a jihar Imo har sai wani lokaci.

Ta kuma yi barazanar katse aiki a faɗin Najeriya har sai hukumomi sun ɗauki matakan gaggawa na tabbatar da tsaron ma’aikatan lantarki a faɗin ƙasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp