Home Labarai Na kadu matuka da sace Dalibai ‘yan mata a jihar Kebbi –...

Na kadu matuka da sace Dalibai ‘yan mata a jihar Kebbi – Tinubu

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya ce yana takaicin sace ƴan matan da aka yi a Kebbi, da kuma alhinin mutuwar Birgadiya Janar Musa Uba da gwarazan sojojin da suka mutu a jihar Borno.

A cikin wani saƙon da ya wallafa a shafinsa na X, Tinubu ya ce ya shiga matuƙar damuwa kan mutuwar sojojin ƙasar da ke bakin aiki.

Ya kuma miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan waɗanda suka rasu, da kuma saƙon jaje da iyayen ɗaliban da aka sace, inda ya ce yana ci gaba da yi musu addua.

” Ina cikin damuwa sosai kan yadda ƴan bindiga suka katse wa ƴan matan nan karatunsu, na umurci jam’ian tsaro su yi gaggawar dawo da ƴan matan gida” ” Ina sane da ƙaruwar rashin tsaro a wasu sassan ƙasar, kuma na bai wa jami’an tsaro umurnin daƙile matsalolin cikin gaggawa”. a cewar shugaban.

Ya kuma yi kira ga ƴan ƙasar da su taimaka wa jam’ian tsaro wajen basu haɗin kai da kuma bayanai masu muhimmanci, inda ya sha alwashin hukunta masu yi wa tsaron ƙasar barazana.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp