Home Labarai Dalibai 24 da ‘yan bindiga suka sace a Kebbi sun shaƙi iskar...

Dalibai 24 da ‘yan bindiga suka sace a Kebbi sun shaƙi iskar ‘yanci

Gwamnatin Najeriya ta sanar da cewa, jami’an tsaro sun samu nasarar ceto ɗalibai mata 24 da ‘yan bindiga suka sace a makarantar sakandiren Maga dake jihar Kebbi a makon da ya gabata.

A ranar 17 ga watan Nuwamba da sanyin safiya ne ‘yan bindigar su ka kai hari makarantar tare da yin garkuwa da ‘yan matan, ‘yan sa’o’i bayan barin dakarun ƙasar daga yankin.

Harin na Kebbi ya ta’azzara matsalar tsaro a Najeriya, inda wasu mahara na daban suka afkawa yankin Eruku na Kwara tare da sace masu ibada kodayake an samu nasarar ceto dukkaninsu.

Haka zalika, Ƙungiyar Kiristocin Najeriya ta ce 50 daga cikin ɗalibai fiye da 300 da ‘yan bindiga suka sace a makarantar Katolika dake Neja sun shaƙi iskar ‘yanci.

Shugaba Tinubu ya yabawa jami’an tsaron ƙasar da ƙoƙarin da su ke yi, tare da kira na su jajirce don ceto suaran ɗaliban da har yanzu ke hannun ‘yan bindiga.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp