Home General NDLEA ta cafke miyagun ƙwayoyi da darajarsu ta haura naira biliyan 6

NDLEA ta cafke miyagun ƙwayoyi da darajarsu ta haura naira biliyan 6

Hukumar hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyi ta NDLEA a Najeriya, ta bankaɗo muggan ƙwayoyi da aka ɓoye a wasu manyan ɗakunan ajiyar kayayyaki da kuɗinsu suka tasama sama da naira biliyan shida da miliyan 700 a jihar Lagos.

Wata sanarwa da daraktan sashen yaɗa labarai na hukumar, Femi Babafemi ya fitar tace, yayin samamen da jami’an NDLEA ɗin suka gudanar, sun kuma cafke wani babban dillalin ƙwaya mai suna Onyekachi Pius tare da wasu mutum biyar.

Sanarwar ta ci gaba da cewa, an samu mutanen da aka cafke ɗauke da waɗannan ƙwayoyi a tattare da su, bayan samamen da aka kai maɓoyarsu da ke wani rukunin gidajee da ke Lagos.

Daga cikin kayayyakin da aka gano a hannun su, akwai maganin Tramadol da kuma kodin, wanda ake zargin sun adana ne saboda bikin Kirismeti da ke ƙaratowa.

A cewar NDLEA, manyan motoci aka yi amfani da su wajen fitar da tarin waɗannan muggan ƙwayoyin daga rukunin gidaje na Festac da ke yankin Apple Junction.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp