Home Labarai Gwamnatin jihar Kebbi ta damka daliban da aka kubutar hannun iyayensu

Gwamnatin jihar Kebbi ta damka daliban da aka kubutar hannun iyayensu

Gwamnatin jihar Kebbi ta mika daliban makarantar ‘yan mata ta Maga da aka kubutar daga hannu ýan bindiga su 24 ga iyayensu.

Wannan dai ya gudana ne bayan wani kwarya-kwaryar biki da aka gudanar, wanda yake cike da adduóin neman zaman lafiya da ingantaccen tsaro a birnin kebbi, wanda gwamantin jihar ta shirya domin sake hada yaran da iyayen nasu.

Bikin ya gudana ne karkashin kulawar kwamishin ilimi ta jihar Hajiya Halima Bande, wadda ta nuna damuwarta bisa halin da yaran da iyayen su suka shiga na tashin hankali.

Da take jawabi a wajen taron matar gwamnan jihar Hajiya Zainab Nasare Idris ta bukaci iyayen yaran da kada wannan dalilin yasa su yi watsa da yin karantun ‘ya’ya mata wanda hakan ka iya mayar da hannun agogo baya.

A makon jiya ne aka tashi da labarin cewa ‘yan bindiga dauke da muggan makamai sun yi awun gaba da ɗaliban sakandiren Maga su 25 a yankin  karamar hukumar Danko-Wasagu da ke jihar Kebbi, inda suka kashe mutum biyu a makarantar.

Ana tsaka da jimamin satar ɗaliban kwatsam sai aka tashi kuma da labarin garkuwa da ɗalibai sama da 250  a makarantar sakandiren St Mary da ke garin Kwantagora na jihar Neja.

Baya ga waɗannan, masu ɗauke da makaman sun gudanar da mabanbantan hare-hare tare da awun gaba da mutane a jihohin Kwara da Sokoto da kuma Kano.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp