Home Labarai Gwamnatin jihar Kebbi ta damka daliban da aka kubutar hannun iyayensu

Gwamnatin jihar Kebbi ta damka daliban da aka kubutar hannun iyayensu

Gwamnatin jihar Kebbi ta mika daliban makarantar ‘yan mata ta Maga da aka kubutar daga hannu ýan bindiga su 24 ga iyayensu.

Wannan dai ya gudana ne bayan wani kwarya-kwaryar biki da aka gudanar, wanda yake cike da adduóin neman zaman lafiya da ingantaccen tsaro a birnin kebbi, wanda gwamantin jihar ta shirya domin sake hada yaran da iyayen nasu.

Bikin ya gudana ne karkashin kulawar kwamishin ilimi ta jihar Hajiya Halima Bande, wadda ta nuna damuwarta bisa halin da yaran da iyayen su suka shiga na tashin hankali.

Da take jawabi a wajen taron matar gwamnan jihar Hajiya Zainab Nasare Idris ta bukaci iyayen yaran da kada wannan dalilin yasa su yi watsa da yin karantun ‘ya’ya mata wanda hakan ka iya mayar da hannun agogo baya.

A makon jiya ne aka tashi da labarin cewa ‘yan bindiga dauke da muggan makamai sun yi awun gaba da ɗaliban sakandiren Maga su 25 a yankin  karamar hukumar Danko-Wasagu da ke jihar Kebbi, inda suka kashe mutum biyu a makarantar.

Ana tsaka da jimamin satar ɗaliban kwatsam sai aka tashi kuma da labarin garkuwa da ɗalibai sama da 250  a makarantar sakandiren St Mary da ke garin Kwantagora na jihar Neja.

Baya ga waɗannan, masu ɗauke da makaman sun gudanar da mabanbantan hare-hare tare da awun gaba da mutane a jihohin Kwara da Sokoto da kuma Kano.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp