Home Labarai Gwamnatin jihar Kebbi ta damka daliban da aka kubutar hannun iyayensu

Gwamnatin jihar Kebbi ta damka daliban da aka kubutar hannun iyayensu

Gwamnatin jihar Kebbi ta mika daliban makarantar ‘yan mata ta Maga da aka kubutar daga hannu ýan bindiga su 24 ga iyayensu.

Wannan dai ya gudana ne bayan wani kwarya-kwaryar biki da aka gudanar, wanda yake cike da adduóin neman zaman lafiya da ingantaccen tsaro a birnin kebbi, wanda gwamantin jihar ta shirya domin sake hada yaran da iyayen nasu.

Bikin ya gudana ne karkashin kulawar kwamishin ilimi ta jihar Hajiya Halima Bande, wadda ta nuna damuwarta bisa halin da yaran da iyayen su suka shiga na tashin hankali.

Da take jawabi a wajen taron matar gwamnan jihar Hajiya Zainab Nasare Idris ta bukaci iyayen yaran da kada wannan dalilin yasa su yi watsa da yin karantun ‘ya’ya mata wanda hakan ka iya mayar da hannun agogo baya.

A makon jiya ne aka tashi da labarin cewa ‘yan bindiga dauke da muggan makamai sun yi awun gaba da ɗaliban sakandiren Maga su 25 a yankin  karamar hukumar Danko-Wasagu da ke jihar Kebbi, inda suka kashe mutum biyu a makarantar.

Ana tsaka da jimamin satar ɗaliban kwatsam sai aka tashi kuma da labarin garkuwa da ɗalibai sama da 250  a makarantar sakandiren St Mary da ke garin Kwantagora na jihar Neja.

Baya ga waɗannan, masu ɗauke da makaman sun gudanar da mabanbantan hare-hare tare da awun gaba da mutane a jihohin Kwara da Sokoto da kuma Kano.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp