Home Labarai Sojojin Nijeriya sun kubutar da Yara mata 12 daga hannun mayakan ISWAP...

Sojojin Nijeriya sun kubutar da Yara mata 12 daga hannun mayakan ISWAP a Borno

Sojojin  Nijeriya karkashin dakarun rundunar OPERATON HADIN KAI sun sami nasarar kubutar da yara mata 12 da mayakan kungiyar boko haram suka yi garkuwa da su a kauyen Mussa dake karamar hukumar Askira/Uba dake jihar Borno a Arewa aso gabashin Nijeriya.

Mayakan boko haram sun yi garkuwa da yaran ne a lokacin da suke girbe amfanin gonarsu a ranar 23 ga watan Nuwamba, wanda kuma suka shaki iskan ‘yanci a ranar 29 ga watan na Nuwamba bayan abinda dakarun sojin suka bayyana samun bayanan sirri da kuma ayyukan kakkabe matsalar tsaro a yakin kudancin jihar.

Ta cikin wata sanarwa da rundunar sojin ta aikewa PRNigeria ta bayyana cewa wadanda aka kubutar din dake mata ne kuma suna karbar kulawar likitoci domin tallafawa lfiyarsu kamar yadda ya kamata. Wanda nan ba da jimawa ba za’a sadasu da iyalansu.

Yaran da aka kubutar suna hadar da  Fatima Shaibu (17), Fatima Umaru (15), Hauwa Abubakar (18), Saliha Muhammed (15), Sadiya Umaru (17), Amira Babel (15), Zara Adamu (17), Nana Shaibu (15), Zainab Musa (18), Zainab Muhammed (17), Jamila Saidu (15), and Hauwa Hamidu (17).

Rundunar Sojin ta yabawa dakarun nata bisa namijin kokarin da uke nunawa a yaki da matsalar tsaro a yankin, sannan ta bukaci Al’ummar dake jihar su sake sanya idanu gami da taimakawa jami’an tsar da bayanan sirri.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp