Home Labarai An ceto wasu daga cikin daliban da aka sace a makarantar Papiri...

An ceto wasu daga cikin daliban da aka sace a makarantar Papiri da ke jihar Neja

Gwamnatin tarayya ta tabbatar da ceto ɗalibai 100 daga cikin mutum 315 da ’yan bindiga suka sace a Makarantar St. Mary’s da ke Papiri, ƙaramar hukumar Agwara a Jihar Neja.

’Yan bindigar sun kai farmakin ne a ranar 21 ga Nuwamba, 2025, inda suka mamaye makarantar suka tafi da mutum 315 da suka haɗa ɗalibai 303 da malamai 12.

Rahotanni sun nuna cewa jami’an tsaro tare da mafarauta na yankin sun bazama cikin dazuzzukan da ke makwabtaka da Papiri domin neman waɗanda aka sace.

A rana ta farko bayan harin, yara 50 sun yi nasarar tserewa kuma suka koma hannun iyalansu lamarin da ya kawo addadin waɗanda suka rage a hannun ƴan bindigar zuwa mutum 265 kafin wannan sabon cigaba na ceto wasu daga cikinsu.

Gwamnatin Jihar dai ta bayyana cewa kafin aukuwar lamarin ta samu sahihan bayanan sirri game da yiwuwar tashin hankula a sassan Neja ta Arewa, saboda haka ta dakatar da ayyukan gine-gine tare da rufe makarantu masu kwana a yankunan da abin ya shafa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp