Home General Har yanzu sojojin Najeriya 11 na Burkina Faso – Tugga

Har yanzu sojojin Najeriya 11 na Burkina Faso – Tugga

Ministan harkokin wajen Najeriya, Yusuf Tuggar, ya ce har yanzu sojojin Najeriya 11 na maƙale a ƙasar Burkina Faso bayan saukar gaggawa da wani jirgi da suke ciki ya yi a ƙasar.

Rahoton ya ce lamarin ya faru ne tun ranar 8 ga Disamba, lokacin da jirgin ya yi saukar gaggawa a ƙasar inda ƙungiyar ƙasashen Sahel (AES) ta zargi jirgin sojin Najeriya da keta sararin samaniyar Burkina Faso ba tare da izini ba.

A cewar rahoton, shugaban gwamnatin soji ta Mali, Assimi Goïta, ya bayyana saukar jirgin a matsayin matakin da ya saɓa wa ƙa’idojin ƙasashen duniya

Rundunar Sojin Saman Najeriya kuwa ta ce jirgin yana kan hanyarsa ce ta zuwa ƙasar Portugal lokacin da ya samu tangarɗar na’urar da ta tilasta masa yin saukar gaggawa a ƙasar.

Kungiyar AES – ta ƙunshi ƙasashen Burkina Faso da Mali da Nijar wadanda suka fice daga ƙungiyar ECOWAS a watan Janairu, bayan takunkuman da aka sanya musu sakamakon juyin mulki a ƙasashensu.

Sun sanar da ficewarsu daga ƙungiyar ne a daidai lokacin da Najeriya ke jagorantar ECOWAS.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp