Home Labarai APC ta yi watsi da yunƙurin tsige Gwamna Fubara

APC ta yi watsi da yunƙurin tsige Gwamna Fubara

Jam’iyyar APC reshen jihar Rivers ta yi fatali da yunƙurin tsige gwamnan jihar, Siminalayi Fubara da majalisar dokokin jihar ke shirin yi.

Cikin wata sanarwa da APC ta fitar ta ce duk da cewa tana girmama cin gashin kan majalaisar dokoki, amma ba za ta amince da yunƙurin tsige gwamnan ba.

A ranar Alhamis ne majalisar dokokin jihar da ke kudu maso kudancin Najeriya ta ƙaddamar da yunƙurin sake tsige gwamnan da mataimakiyarsa, Ngozi Odu, saboda zarginsu da laifukan da suka saɓa ƙa’idar aiki.

Jam’iyyar APC da ke mulkin jihar ta bayyana shirin da yunƙurin ”tayar da hargisti” a jihar.

APC ta kuma yi kira ga mambobin majalisar dokokin jihar su kauce wa duk wani yunƙuri da zai jefa jihar cikin rikicin siyasa.

A watan da ya gabata ne dai Gwamna Fubara ya koma APC bayan ficewarsa daga PDP.

Tun bayan zaɓen 2023, jihar – mai arzikin man fetur – ta faɗa rikicin siyasa sakamakon saɓanin da gwamnan jihar Siminalayi Fubara ya samu da ministan Abuja, wanda shi ne tsohon gwamnan jihar Nysome Wike.

Ricikin ya ci gaba da ƙamari, lamarin da ya kai ga shugaban ƙasar, Bola Tinubu ayyana dokar ta-ɓaci a jihar tare da dakatar da Gwamnan Fubara har na tsawon wata shida a shekarar da ta gabata.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp