Home Labarai Gwamnatin Najeriya ta dakatar da fara aikin sabuwar dokar haraji

Gwamnatin Najeriya ta dakatar da fara aikin sabuwar dokar haraji

Gwamnatin Najeriya ta dakatar da tsare-tsare da za a yi amfani da su wajen aiwatar da sabbin dokokin haraji, tana mai kafa hujja da wasu rashin tabbas kan matakan ƙarshe da aka bijiro da su cikin sabuwar dokar.

Shugaban Kwamitin Shugaban Ƙasa kan tsarin harajin, Taiwo Oyedele ne ya bayyana hakan yayin wata ganawa da manema labarai a birnin Legas, yana mai cewa akwai nazarce-nazarce da ya kamata a kammala bibiya kafin fara aiwatar da dokar.

Oyedele ya ce tuni ya shaida wa hukumomin da ke da ruwa da tsaki a ɓangaren haraji su dakata da duk wani aiki da ya shafi wannan doka.

Dokar haraji ta Najeriya, wadda ta fara aiki a ranar 1 ga Janairu, ta fuskanci suka bayan zargin cewa anyi sauye-sauye da majalisar dokokin ƙasar ta amince da su, akwai ɗungushe a ciki.

Sai dai Oyedele ya nuna damuwa kan yadda wannan mataki ke fuskantar caccaka, yana mai danganta hakan da yaɗa labaran ƙarya da nufin kawo cikas ga sabon tsarin harajin.

Ya ce yadda aka riƙa yamaɗiɗin labaran ƙarya a bara, hakan ya sanya Najeriya yin asarar Naira tiriliyan 4.6 a rana guda cikin watan Nuwamba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp