Home Labarai Gwamnatin Najeriya ta dakatar da fara aikin sabuwar dokar haraji

Gwamnatin Najeriya ta dakatar da fara aikin sabuwar dokar haraji

Gwamnatin Najeriya ta dakatar da tsare-tsare da za a yi amfani da su wajen aiwatar da sabbin dokokin haraji, tana mai kafa hujja da wasu rashin tabbas kan matakan ƙarshe da aka bijiro da su cikin sabuwar dokar.

Shugaban Kwamitin Shugaban Ƙasa kan tsarin harajin, Taiwo Oyedele ne ya bayyana hakan yayin wata ganawa da manema labarai a birnin Legas, yana mai cewa akwai nazarce-nazarce da ya kamata a kammala bibiya kafin fara aiwatar da dokar.

Oyedele ya ce tuni ya shaida wa hukumomin da ke da ruwa da tsaki a ɓangaren haraji su dakata da duk wani aiki da ya shafi wannan doka.

Dokar haraji ta Najeriya, wadda ta fara aiki a ranar 1 ga Janairu, ta fuskanci suka bayan zargin cewa anyi sauye-sauye da majalisar dokokin ƙasar ta amince da su, akwai ɗungushe a ciki.

Sai dai Oyedele ya nuna damuwa kan yadda wannan mataki ke fuskantar caccaka, yana mai danganta hakan da yaɗa labaran ƙarya da nufin kawo cikas ga sabon tsarin harajin.

Ya ce yadda aka riƙa yamaɗiɗin labaran ƙarya a bara, hakan ya sanya Najeriya yin asarar Naira tiriliyan 4.6 a rana guda cikin watan Nuwamba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp